Asibitin dawanau ya ce Sheikh Abduljabbar ba shi da matsalar kwakwalwa

Abduljabbar

Asibitin masu fama da matsalar kwakwalwa na Dawanau da ke jihar Kano a arewacin Najeriya ya ce Abduljabbar Kabara ba shi da matsalar kwakwalwa.

A ci gaba da zaman sauraren ƙarar malamin da ake yi, duka lauyoyin Abduljabbar ba su halarci zaman kotun ba na ranar Alhamis.

Wakilin BBC da ya halarci zaman kotun ya ce lauyan Abduljabbar daya ne ya je kotun Barista Haruna Magashi kuma take ya ce ya janye daga wakiltar malamin.

Ya kuma ce “Sauran lauyoyin su ma sun janye daga kare Abduljabbar shi ya sa dukkansu babu wanda ya halarci zaman kotun.

A bayanin sakamakon gwajin asibitocin da aka gabatar wa kotun, Asibitin Dawanau na masu matsalar kwakwalwa ya ce an taɓa kwantar da Abduljabbar a asibitin na tsawon kwana hudu a baya.

“Lokacin da ya taÉ“a yin rikici da ‘yan uwansa an taÉ“a kwantar da shi a asibitin na kwana hudu, amma ba a taÉ“a yi masa gwaji ba kuma ba a taÉ“a ba shi magani ba,” in ji mai karanto bayani a gaban kotun.

Alkali Ibrahim Sarki Yola wanda ke yin shari’ar, ya tambayi sakamakon Asibitin Murtala da aka kai Abduljabbar domin yi masa gwajin kunne, saboda gaza amsa tambayoyin da aka yi masa a zaman kotun na baya, wanda ake tsammanin ko ya samu matsalar kunne ne.

“A sakamakon gwajin kunnen da muka samu daga Asibitin Murtala, an tabbatar da cewa Abduljabbar ba shi da matsalar kunne ko kuma ji ko kaÉ—an,” mai gabatar da bayani ya ce.

Alƙali Yola ya ce ya amince da buƙatar lauyoyin Abduljabbar na janye wa daga kare malamin.

An ɗage sauraren ƙarar Malamin zuwa ranar 30 ga watan Satumbar 2021.

Matashiya

A ranar 2 ga watan Satumbar da muke ciki ne wata Kotun Musuluncin da ke shari’ar Malamin ta umarci a yi masa gwajin kwakwalwa da kunne a wani zaman ci gaban shari’ar da aka yi.

Kotu ta bayar da umarnin ne bayan malamin addinin Musuluncin ya gaza amsa tambayoyin da alkalin kotun Mai Shari’a Sarki Ibrahim Yola ya yi masa ranar 2 ga watan.

Lauyoyin da ke kare Abduljabbar karkashin jagorancin Barista Sale Bakaro sun soki yadda ake tsawaita shari’ar da kuma sabbin tuhume-tuhumen da aka gabatar kan Malamin.

Sai dai Alkali Sarki Ibrahim Yola ya ce a fahimtarsa wadannan tuhume-tuhume da aka gabatar wajibi ne domin a karanta wa wanda ake zargi laifukan da ake bukatar amsa daga gare shi.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...