An sako sufeta bayan biyan miliyan 2 a matsayin kudin fansa – AREWA News

Insifectan yan sanda da aka bayyana da Sylve da kanin tsohon shugaban karamar hukumar Kuje,Alhaji Muhammad A. Galadima da kuma Nengbe Mundi sun samu yancin kansu ne bayan da suka biya kudin fansa miliyan ₦2 ga mutanen da suka yi garkuwa da su.

Mutanen uku an yi garkuwa da su a ranakun Juma’a da kuma Asabar din da suka wuce, a garin Rubochi dake karamar hukumar .

Wani daga cikin iyalinsu da ya nemi a boye sunansa, ya tabbatar da sakin jami’in dan sandan da kuma sauran mutane biyun da aka yi garkuwa da su.

Ya ce an sako mutanen ne da misalin karfe 11 na dare bayan da masu garkuwar suka karbi naira miliyan daya kudin fansar kanin shugaban karamar hukumar,₦550,000 na jami’in dan sandan da kuma ₦400,000 na Nengba Mundi.

A cewarsa an kai kudin fansar ne wani daji dake kusa da kauyen Ggowodi a karamar hukumar Toto ta jihar Nasarawa.

Ya kuma ce an saya musu katin waya na Glo har na ₦30,000, sinkin kwalin taba Aspen da kuma katan guda na maganin Boska.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...