An Saki Sunday Igboho Daga Gidan Yari A Kasar Benin

Adeyemo wanda aka fi sani da suna Sunday Igboho, dan kabilar Yarbawa ne kuma ya yi fice tare da yin kira da a fatattake makiyaya daga kabilar Fulani daga kasashen Yarbawa a kudu maso yammacin Najeriya.

An kama shi ne a watan Yulin da ya gabata a filin jirgin saman Cotonou lokacin da yake kan hanyar zuwa Jamus, bayan da wata hukumar tsaron Najeriya ta ce ta gano tarin makamai a gidansa.

An sake shi ne a yammacin ranar Litinin din da ta gabata saboda dalilai na lafiyar jikinsa, tare da sharadin ba zai iya barin kasar Benin ba, in ji daya daga cikin lauyoyinsa da ya bukaci a sakaya sunansa har sai an gudanar da taron manema labarai.

Mukarraban sa ne kawai za a ba su damar shiga gidansa da ke Cotonou babban birnin kasuwancin Benin, wanda ‘yan sanda za su sanya ido a kai, in ji lauyan.

Kame Igboho dai ana kallonsa a matsayin wata alama ta kara zafafa kokarin gwamnatin Najeriya na bin mutanen da ake ganin barazana ce ga tsaron kasa, har da fiye da kan iyakokinta.

Hakan ya zo ne jim kadan bayan da shugaban ‘yan awaren Nnamdi Kanu, daga kabilar Igbo da ke da tushe a kudu maso gabashin Najeriya, aka dawo da shi Najeriya bisa zarginsa da ta’addanci, kashe-kashen mutane da cin amanar kasa. Kanu da lauyoyinsa sun ce an tsare shi kuma an cin zarafinsa a Kenya ba bisa ka’ida ba kafin a mika shi, lamarin da Kenya da Najeriya suka musanta.

Tun da farko dai kafafen yada labarai sun ce Najeriya na neman a mika Igboho, amma ba a san halin da wannan bukata ta ke ciki ba. Hukumomin Najeriya dai ba su amsa bukatur yin tsokaci kan lamarin Igboho ba.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...