Ƴan bindiga sun buɗe wuta kan motar kulob ɗin Sunshine Stars

Ƴan wasa da kuma jagororin kungiya ne suka jikkata a wani hari da ƴan bindiga suka kai kan tawagar kungiyar kwallon kafa ta Sunshine Stars dake Akure.

Ƴan bindigar sun bude wuta ne kan motar kungiyar kwallon kafar akan hanyar Benin-Ore.

Acikin wata sanarwa, Michael Akintunde jami’in hulɗa da jama’a na kungiyar ya ce an kai harin ne da maraicen ranar Alhamis.

Ya ce tawagar ƴan wasan na kan hanyar zuwa Benin ne domin buga wasan mako na 13 na gasar kungiyoyin kafa ajin kwararru ta NPFL da kungiyar Bendel Insurance dake Benin.

Akintunde ya ce babu wanda ya rasa ransa a harin sai waɗanda suka jikkata.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...