Gwamnatin Iran ta rufe birnin Tehran daga Asabar zuwa Talata domin gudanar da jana’izar jagoran addinin kasar, Ayatolla Ali Khamenei.
Mahukunta sun ayyana Talata a matsayin ranar hutu domin bai wa miliyoyin mutane damar halartar jana’izar, inda ake sa ran fiye da mutum miliyan 10 za su taru.
Rahotanni sun bayyana cewa dubban mutane sun kwashe sa’o’i suna jiran fara addu’o’in jana’izar, yayin da magoya bayan Khamenei suke daga jajayen tutoci domin nuna kira ga ramuwar gayya.
Wasu daga cikin mahalarta jana’izar sun bayyana cewa sun fito ne saboda kauna da girmamawa ga marigayin, wanda ya jagoranci Iran tun shekarar 1989.
Masu sharhi a Iran sun ce mutuwar Khamenei ta haddasa hadin kai a tsakanin magoya bayansa, yayin da wasu suka bayyana cewa tsarin mulkin da ya kafa ya taimaka wajen tabbatar da dorewar gwamnati duk da kalubalen tsaro da rikice-rikice.
An Rufe Tehran Yayin Jana’izar Khamenei A Iran

