An matsa wa gwanatin Ganduje lamba ta yi dokar kare yara.

Kungiyoyim fararen hula a jihar Kano da ke arewacin Najeriya na ci gaba da matsin lambar neman gwamnatin Ganduje ta samar da dokar da za ta rika bin kadin hakkin kananan yara, biyo bayan sacewa tare da kashe Hanifa Abubakar da malamin makarantarsu Abdulmalik Muhammad Tanko ya yi.

Zainab Nasir na cikin wadanda suka yi wannan kiran kuma ta shaida wa manema labari cewa akwai bukatar a samar da wata cibiya ta neman karewa da kuma kwatar hakkin yara a Kano.

Ta kara da cewa a kuma rika bibiyar halin da makarantu masu zaman kansu suke ciki domin kaucewa kara faruwar irin wannan lamari, kuma wanda ake zargi da aikata wannan aiki a yi masa hukuncin da doka ta tanada.

Ta kuma ce jan kaar da ake yi wajen samar da wannan doka, yana kara bayar da damar aikata miyagun laifuka ga yara kanana kamar wanda aka shaida a yanzu, tana kuma shawartar gwamnati ta hanzartar zartar da wannan doka a matsayin almarin gaggawa.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...