Wasu mutane da ba a san ko suwaye ba sun cinna wuta a ofishin hukumar zabe ta INEC dake karamar hukumar Igboeze North a jihar Enugu.
An ka hari ofishin hukumar zaɓen ne da misalin karfe 11: 48 na daren ranar Lahadi.
Kwamishinan zabe na jihar Enugu,Emeka Ononamadu ya bayyana cewa duk da cewa ba a samu asarar rayuka ba a harin wutar ta kone a akwatunan zabe 748 da kuma akwakun kada kuri’a 240.
Duk da cewa babu wata kungiya da ta dauki alhakin harin sai dai yayi kama da irin wanda Æ´aÆ´an kungiyar IPOB suke kai wa a yankin kudu maso gabas.