An kona ofishin INEC a Enugu

Wasu mutane da ba a san ko suwaye ba sun cinna wuta a ofishin hukumar zabe ta INEC dake karamar hukumar Igboeze North a jihar Enugu.

An ka hari ofishin hukumar zaɓen ne da misalin karfe 11: 48 na daren ranar Lahadi.

Kwamishinan zabe na jihar Enugu,Emeka Ononamadu ya bayyana cewa duk da cewa ba a samu asarar rayuka ba a harin wutar ta kone a akwatunan zabe 748 da kuma akwakun kada kuri’a 240.

Duk da cewa babu wata kungiya da ta dauki alhakin harin sai dai yayi kama da irin wanda ƴaƴan kungiyar IPOB suke kai wa a yankin kudu maso gabas.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]