Amirka ta musanta kai wa sojin Iran hari

Rouhani da Trump


Shugaba Rouhani da Trump sun samu sabani tun bayan janyewar Amirka daga yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015

Amurika ta nisanta kanta da zargin da shugaban Iran Hassan Rouhani ya yi na cewa Washington da kawayenta na yankin gabas ta tsakiya na da hannu a harin da aka kai wanda ya yi sanadiyar mutuwar sojoji da dama.

An dai kai harin ne a birnin Ahvaz kan sojojin kasar ta Iran.To sai dai tuni wasu kungiyoyi suka dauki alhakin kai harin.

Jakadan Amurika a Majalisar Dinkin Duniya, Nikki Haley ta sanar da cewa kamata ya yi shugaba Rouhani ya yi kyakkyawan nazari kafin ya dora alhakin harin kan Amurika.

Haley ta zargi shugaban na Iran da mai mulkin mulaka’u da ya bar al’ummar kasar shi cikin kangi na tsawon lokaci.

A na shi bangare, Anwar Gargash, wani minista na daya daga cikin kasashen yankin daular larabawa ya danganta kalaman na Tehran a matsayin wadanda basu da tushe barae makama.

Wata kabila daga cikin kabilun larabawa ‘yan aware da kuma kungiyar musulmi masu fafutuka da makamai ,dsu ne suka dauki alhakin kai harin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 25.

Reshen kungiyar musulmi masu fafutuka da makamai wato IS mai kulla da farfaganda wato AMAQ ta nuna bidiyon wasu mutane 3 a cikin mota da sukai ikirarin su ne suka kai harin, bidiyon ya nuna suna kan hanyar zuwa birnin Ahvaz inda suka aika barnar.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...