Wani babban jami’in sojin Iran, Mohammad Jafar Asadi, ya bayyana cewa akwai yiwuwar sake ɓarkewar yaƙi tsakanin ƙasarsa da Amurka.
Kamfanin dillancin labarai na Fars ya rawaito Asadi, wanda mamba ne a rundunar sojin Iran ta ‘Khatam al-Anbiya command center’, yana cewa, “Akwai yiwuwar ɓarkewar sabon yaƙi tsakanin Iran da Amurka, kuma alamomi da dama sun tabbatar da cewa Amurka ba ta shirya wa amincewa da kowane irin alƙawari ko yarjejeniya ba”.
Wannan na zuwa ne bayan tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya soki buƙatun da Iran ta gabatar domin tattaunawar zaman lafiya a baya-bayan nan.
A wani ɓangare kuma, mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya bayyana cewa ƙasarsa na a shirye domin tattaunawar zaman lafiya ko kuma komawa yaƙi, dangane da yadda al’amura za su kasance.
Akwai Yiwuwar Sake Barkewar Yaki Tsakanin Iran Da Amurka – Jami’in Soji

