Abin da ya sa Twitter bai samu yadda yake so ba a Najeriya

A woman in Nigeria looking at Twitter on a mobile phone - archive shot

Asalin hoton, AFP

A jerin maƙalolinmu daga marubuta ƴan Afrika, ƴar jaridar Najeriya kuma marubuciya Adaobi Tricia Nwaubani ta duba ƙarfin ikon Twitter da matakin gwamnatin Najeriya na son kawo karshensa.

Yanzu wata biyu kenan tun da gwamnatin Najeriya ta haramta amfani da Twitter bayan da kamfanin na fasaha ya cire wasu saƙonni da Shugaba Muhammadu Buhari ya wallafa inda kamfanin ya ce saƙon ya saɓa dokokinsa na amfani da kalaman ɓatanci.

Duk da ka-ce-na-ce da ya biyo bayan haka a faÉ—in duniya, ciki har da kausasan kalaman alla-wadai daga manyan jami’an diflomasiyyar Æ™asashen waje da ke Æ™asar, gwamnatin ta tsaya kan bakanta.

Sai dai ranar Laraba ta sanar da cewa tana gabar ƙarshe ta sasantawa da Twitter kuma za a dage haramcin nan da ƴan kwanaki ko makonni.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,
Ƴan Najeriya da dama sun fusata da haramta amfani da Twitter a ƙasar

Mafi yawan ce-ce-ku-cen da ya biyo bayan haramcin ya mayar da hankali ne kan illar haramcin kan Æ´ancin bayyana ra’ayi da na tattalin arziki.

Ƴan Najeriya da yawa suna amfani da shafin ne wajen bayyana É“acin ranzu game da gwamnati da kuma mu’amala da abokan kasuwancinsu.

Amma matakin Twitter na cire saÆ™on Shugaba Buhari- wanda ya yi barzanar amfani da karfi kan masu iÆ™irarin É“allewa daga Najeriya – ya zo a lokacin da bai dace ba. Wannan ya zama wani tushe ne muhawara a sassan duniya, ciki har da Indiya.

Kamfanin na Amurka mai zaman kansa ya nuna kamar yana shiga al’amuran cikin gidan Najeriya ba tare da wani isasshen sani kan tarihinta ba balle ya san abin da matakin nasa zai haifar.

Sabon salon mulkin mallaka

A lokacin, Twitter ya ce sakon na shugaban ya saɓa wa dokokinsa.

Kamfanin na da damar amfani da dokokinsa, amma Shugaba Buhari ya wallafa wannan bayanin ne don isar da sako a matsayinsa na Shugaban Najeriya zuwa ga mutanensa inda ya yi amfani da shafin gwamnati.

Kuma an wallafa sakon a sauran shafukan sada zumunta a fadin ƙasar.

Dai-dai ne wani kamfanin Amurka mai zaman kansa ya samu ikon sauyawa, ba tare da izini ba, sako a hukumance na shugaban wata ƙasa a Afrika da aka zaba ta hanyar demokuraɗiyya? Wannan ba komai ba ne illa tsabar sabon salon mulkin mallaka.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,
Shugaba Muhammadu Buhari mai shekaru 78 na mulkin Najeriya tun 2015

Ƴan Najeriya na da ƴancin sanin shiri da manufofin shugabansu, ko da kuwa kalamansa ba su dace ba. Suna da ƴancin sani idan yana shirin kai masu mummunan hari.

Haka kuma, ƴan Najeriya na da ƴancin mayar masa da martani a wani ɓangare na sadarwa tsakanin gwamnati da ƴan ƙasarta.

Saƙonnin Buhari sun yi barazanar ɗaukar mataki kan ƴan ƙungiyar IPOB ta ƴan ƙabilar Ibo, wadda ke koƙarin ɓallewa daga Najeriya.

An haramta IPOB a shekarar 2017 – kungiyar ta kai Æ™arar gwamnati kotu kan haramcin kuma ba ta yi nasara ba.

Ruruwa wutar rarrabuwar kai

Yayin da ƴan ƙabilar Ibo da dama ke tunanin ana ware su ta hanyoyi da dama, kamar hana su muƙamai masu muhimmanci a gwamnati, mafi yawansu ba sa goyon bayan muradin Ipob na ɓallewa.

Haka kuma ba sa son tashin hankalin da suke assasawa da sauran ƙabilu- waɗanda shugaban ipob Nnamdi Kanu ke yawan kira da dabbobin dawa.

A watan Fabrairu, Facebook ya rufe shafin Nnamdi Kanu saboda kalaman nuna ƙiyayya amma ya ci gaba da amfani da shafin Twitter.

Goge saƙonnin Buhari, Twitter ya nuna cewa yana goyon bayan Ipob kuma magoya bayan kungiyar ba su bata lokaci ba wajen murnar abin da suka fahimta a matsayin goyon bayan Twitter.

Bayan da gwamnati ta soki wannan lamari a watan Yuni, Twitter ya cire kaɗan daga cikin saƙonnin shugaban Ipob ɗin.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,
Wasu daga cikin Æ´an Ipob na da burin É“allewa daga Najeriya

Haka kuma, shigar Twitter lamarin Najeriya ya rura wutar rarrabuwar kai da ya haifar da zanga-zangar #EndSars ta watan Oktoban 2020 da aka yi kan cin zarafin da Æ´an sanda ke yi.

Ƙungiyoyi daban-daban sun shiga cikin shirya zanga-zangar da aka fara ta intanet kafin daga bisani aka ci gaba a kan tituna a faɗin Najeriya tsawon kusan mako biyu.

Amma lokacin da Twitter ya sanya shuÉ—in maki mai nuna alamar ‘verified’ a kan shafin É—aya daga cikin Æ™ungiyoyin amma bai sa a wasu ba, hakan ya haifar da hamyya mai Æ™arfi a tsakaninsu kuma wasu sun janye gaba É—aya ma daga gangamin.

“Cikin rashin sani, Twitter ya zaÉ“i shugabannin wannan gangami a Najeriya kuma ya Æ™ara rura hamayyar da dama ta fara raba kawuna masu shirya gangamin,” a cewar É—an jaridar Najeriya Ohimai Amaize.

Ƙoƙarin hana yin suka

Kamfanin fasahar ya shiga gonar da ko Æ™wararrun jami’an diflomasiyyar Æ™asashen waje da shugabannin Æ™asashe ke tsoron shiga.

Mutanen waje sun fahimci cewa bai dace su yi gaggawar tsoma baki a harkokin ƙasashen Afrika ba, kamar Najeriya, inda matsalolinta suke da yawa fiye da tsammani.

Suna ci gaba da ɗora alhakin yin wannan kan kungiyoyin ƙasar da suka fi su fahimtar yadda abubuwa ke tafiya a ƙasar.

Matakin Twitter na kafa hedikwatarsa na Afrika ta Yamma a Ghana mataki ne na Æ™ara samar da fahimtar al’adu.

SharuÉ—É—an gwamnatin Najeriya na É—age haramcin sun Æ™unshi sai Twitter ya yi rajistar kamfaninsa a Najeriya kuma wasu daga cikin ma’aikatansa su zauna a Æ™asar.

Gwamnatin Buhari ta nuna rashin girmama dokar Æ™asa da Æ´ancin bayyana ra’ayi, inda aka tsare wasu Æ´an jarida da masu fafutuka don kawai sun soki gwamnati.

Haramta amfani da Twitter gaba ɗaya wani yunƙuri ne na gwamnati na toshe bakin masu suka kuma ƴan Najeriya na da hujjar damuwa game da haka.

Amma yadda babban kamfanin fasahar ya É—auki matakin yanke hukuncin wanda zai yi magana kuma a wane lokaci, abin damuwa ne.

Wannan na cin karo da Æ´ancin bayyana ra’ayi, a lokacin da ake tsananin buÆ™atar muhawara a bayyana a Æ™asar da ke aiki da demokuraÉ—iyya.

Idan matakin gwamnatin Najeriya na haramta amfani da Twitter alama ce ta kama-karya, lallai abin É—aga hankali ne a ce wani Ba’amurke zaune kan kujerarsa ta alfarma a yankin Silicon Valley ya tsoma bakinsa cikin harkokin cikin gidan Æ™asa mai Æ´ancin kanta a nahiyar Afrika.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...