
Idan kuma ba’a sami ganin watan a ranar Talata ba, hakan na nufin watan Ramadan zai yi ‘farilla’, wato za’a yi azumi 30, kana a yi sallar idi a ranar Alhamis, wadda za ta kasance 1 ga watan Shawwal.
To sai dai sanarwar ta bukaci al’ummar Musulmai da su soma duban watan a ranar Talata 29 ga Ramadan, haka kuma a gaggauta kai tabbatacce kuma sashihin rahoton ganin watan ga uban kasa ko hakimi mafi kusa, domin isarwa ga kwamitin duban wata na majalisar sarkin musulmi.
Sanarwar ta ci gaba da cewa mai alfarma sarkin musulmi ya yi kira ga daukacin jama’a da su ci gaba da yin addu’o’in samun zama lafiya da kwanciyar hankali a Najeriya.
A daya bangaren kuma shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari, ya bukaci ‘yan kasar da su yi kaffa-kaffa a bukukuwan sallar idi na bana, kasancewar har yanzu ana cikin annobar COVID-19.
Akan haka ne ma shugaban kasar zai gudanar da sallar idi tare da iyalansu da manyan jami’an gwamnatinsa a cikin fadar shugaban kasa da ke Abuja, tare da bin dukkan sharuda da dokokin yaki da cutar ta korona.
Bayan wannan kuma, an soke kai gaisuwar sallah da bisa al’ada shugabannin addini da na al’umma da ma na siyasa suke kai wa shugaban kasa.