A Kalla Mutane Hudu Sun Mutu Sakamakon Wani Hadarin Jirgin Ruwa A Jihar Taraba

TARABA, NIGERIA – Abdulrazak Abubakar Maito sarkin barjin Ibbi kuma shugaban masu aiki da jiragen ruwa a kwatar Ibbi, ya ce yanzu haka dai an samo gawarwaki biyu, kuma suna neman sauran biyun a cikin kogin, sai dai ba su yi nasara ba tukunna.

Abubakar Aliyu kuma iyalansa su biyu ne suka rasu sakamakon wannan hastari na jirgin ruwa, kuma ya kara da cewa yanzu haka suna cikin tashin hankali sosai saboda aukuwar lamarin.

A Kalla Mutane Hudu Sun Mutu Sakamakon Wani Hadarin Jirgin Ruwa A Jihar Taraba
A Kalla Mutane Hudu Sun Mutu Sakamakon Wani Hadarin Jirgin Ruwa A Jihar Taraba

Shugaban karamar hukumar Ibbin Hon. Dr. Bala S. Bako ya tabbatar da faruwar hatsarin jirgin ruwan, ya kuma yi kira ga gwamnatin Jihar da ta tarayyya Nigeria da su kawo musu agajin gaggawa domin rayuwarsu na cikin hadari a yankin.

Yayin da muke hada wannan rahoton mun nemi jin ta bakin rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba amma haka ba ta cimma ruwa ba.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...