Oshiomhole Ya Zargi Akpabio Da Bai Wa ‘Yarsa Mukami A NNPCL Ba Tare Da Ka’ida Ba



Sanata Adams Oshiomhole ya yi zargin cewa ‘yar Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ta samu wani mukami mai kyau a Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) ba tare da bin tsarin daukar ma’aikata na hukuma ba.

Oshiomhole ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a shirin Mic On Podcast, inda ya ce tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kyari, ne ya taimaka wajen nada ‘yar Akpabio a wannan matsayi.

Ya kuma yi zargin cewa daukar ‘yan uwa da abokan arziki aiki ya zama ruwan dare a cikin NNPCL, inda ya ce wasu jami’ai sun bai wa ‘ya’yansu da danginsu mukamai daban-daban a kamfanin.

Sai dai Sanatan ya jaddada cewa babu matsala idan dangin jami’an gwamnati sun samu aiki a NNPCL, matukar sun cancanta kuma an bi dukkan ka’idojin daukar ma’aikata.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, Akpabio da NNPCL ba su mayar da martani kan zarge-zargen ba.

More from this stream

Recomended