Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da ƙudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke neman kafa rundunar ƴansandan jihohi a faɗin ƙasar.
Amincewar ta biyo bayan shekaru ana muhawara kan hanyoyin da za a bi wajen inganta tsaro da daƙile matsalolin rashin tsaro a Najeriya.
Rahotanni sun ce fiye da kashi biyu bisa uku na sanatoci ne suka kaɗa ƙuri’ar amincewa da ƙudirin bayan nazari kan tanade-tanadensa.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya sanar da amincewar ƙudirin a zaman majalisar na ranar Laraba.
Ɗaya daga cikin tanade-tanaden ƙudirin shi ne bai wa gwamnoni ikon naɗa kwamishinonin ƴansandan jihohinsu, bayan majalisun dokokin jihohi sun tantance tare da amincewa da su.
Wasu gwamnoni da manyan jami’an gwamnatin tarayya sun halarci zaman majalisar lokacin tattaunawar ƙudirin.
Majalisar Dattawa Ta Amince Da Ƴansandan Jihohi

