Gwamnatin Jihar Kogi ta tabbatar da sace yara 24 daga wani gidan marayu a jihar, abin da ya sake jawo damuwa kan matsalar tsaro.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a safiyar ranar Lahadi, 26 ga Afrilu 2026, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kutsa cikin gidan marayun suka tafi da yaran zuwa inda ba a sani ba.
Kwamishinan yada labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya bayyana lamarin a matsayin “abin takaici da tayar da hankali,” yana mai tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro domin kubutar da yaran.
Fanwo ya kara da cewa ana ci gaba da kokarin gano masu laifin, yana mai jaddada cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai an hada yaran da iyalansu da masu kula da su.
Haka kuma rundunar ‘yan sanda ta jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce an fara hadin gwiwar jami’an tsaro daban-daban domin ceto yaran da kuma kama wadanda suka aikata laifin.
Gwamnatin Kogi Ta Tabbatar Da Sace Yara 24 Daga Gidan Marayu

