Isra’ila Ta Fitar Da Gargaɗi Bayan Iran Ta Harba Mata Makamai Masu Linzami



Rundunar sojin Isra’ila (IDF) ta fitar da sabon gargaɗi ga ƴan ƙasar, bayan ta ce ta gano wasu makamai masu linzami da Iran ta harba zuwa cikin ƙasar.

Sanarwar ta ce wannan harin shi ne na biyar da Iran ta kai cikin Isra’ila a cikin sa’o’i tara kacal, lamarin da ya ƙara tayar da hankalin jama’a.

Sojojin Isra’ilar sun buƙaci mazauna wuraren da ake tsammanin makaman za su sauka su garzaya zuwa mafaka domin kare rayukansu.

Hukumomi sun ce suna ci gaba da sa ido kan halin da ake ciki, yayin da ake ƙoƙarin kare yankunan da ake zaton na iya fuskantar barazana.

More from this stream

Recomended