Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci gwamnonin jihohi da shugabannin addinai Musulmi da Kirista da su ƙara tausayi ga talakawa da marasa galihu, ta hanyar tsara manufofin da za su amfanar da jama’a a matakin ƙasa.
Wanna ya fito ne cikin wata sanarwa da ta fito daga mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga.
Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Abuja, yayin da ya karɓi bakuncin gwamnoni domin buɗa-baki na haɗin kan addinai a Fadar Shugaban Ƙasa. Ya ce zuwan watan Ramadan da kuma lokacin Lent a lokaci guda na nuna muhimmancin haɗin kai, sadaukarwa da tausayi tsakanin al’umma.
Ya ƙara da cewa wadannan lokuta suna ba shugabanni damar duba halin da jama’a ke ciki tare da samar da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar talakawa, musamman matasa da marasa aikin yi.
Shugaban ya jaddada cewa dole ne a ƙara ƙoƙari wajen rage talauci da ƙarfafa matasa, yana mai kira ga shugabanni su bai wa kowa dama ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.
Tinubu ya kuma bayyana aniyarsa na kafa ‘yan sandan jihohi domin magance matsalar tsaro a ƙasar, yana mai cewa tsaro shi ne ginshiƙin ci gaba.
A wajen taron, gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, wanda ya wakilci ƙungiyar gwamnonin Najeriya, ya yabawa shugaban ƙasa kan ƙoƙarinsa na haɗa kan ƙasa duk da bambance-bambancen addini da ƙabila.

