Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani matashi mai suna Yusif Malam-Gwani mai shekaru 18, wanda ya nutse a wani buɗaɗɗen tafkin ruwa a yankin Bachirawa, Kwanar Madugu, cikin Ƙaramar Hukumar Ungogo.
Daraktan hukumar, Alhaji Sani Anas, ya bayyana cewa sun samu kiran gaggawa daga wani Sulaiman Abdullahi-Tela a ranar Alhamis da rana cewa matashin ya faɗa cikin ruwan. Nan take aka tura tawagar ceto zuwa wurin, inda aka fito da shi amma tuni ya rasu. Daga bisani an miƙa gawarsa ga shugaban unguwar Bachirawa, Jibrin Isah.
A wani lamari makamancin haka, wani yaro ɗan shekara takwas mai suna Abdussalam Ibrahim ya faɗa rijiya a unguwar Kofar Yamma da ke garin Karaye, cikin Ƙaramar Hukumar Karaye.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi, ya ce sun samu rahoton lamarin daga wani ma’aikacinsu, Murtala Magaji. An tura tawagar ceto nan take, amma shi ma an fito da yaron a mace, sannan aka miƙa gawarsa ga mahaifinsa, Malam Musa-Mudi.
Hukumar ta yi kira ga jama’a da su riƙa ɗaukar matakan kariya a wuraren rijiyoyi da buɗaɗɗun tafkunan ruwa, musamman domin kare rayukan yara.
Ta kuma miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu.
Matashi Da Yaro Ɗan Shekara Takwas A Kano Sun Nutse A Ruwa

