
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi rijistar sababbin jam’iyyun siyasa guda biyu.
Joash Amupitan shugaban hukumar shi ne ya sanar da haka a ranar Alhamis a wurin taron tattaunawa da hukumar tayi da jam’iyyun siyasa a Abuja.
Sababbin jam’iyyun da suka samu rijista su ne Democratic Leadership Alliance (DLA) da kuma Nigeria Democratic Congress (NDC).
Rijistar ta samu ne biyo bayan tantacewa tare da duba dukkanin sharuda da kuma ka’idoji na zama jam’iya.
Hukumar ta ce kungiyoyi 171 ne suka mikawa hukumar takardar buÆ™atar a yi musu rijista a matsayin jam’iyun siyasa.
A cewar shugaban hukumar kungiyoyi 14 suka tsallake matakin farko na cancanta.
” A cikinsu takwas ne kaÉ—ai suka iya É—ora takardun da ake buÆ™ata a shafin intanet na musamman da hukumar ta samar,” a cewar shugaban.
” Jam’iyyun su ne All Democratic Alliance (ADA), Citizens Democratic Alliance (CDA), Abundance Social Party (ASP), African Alliance Party (AAP), Democratic Leadership Alliance (DLA), Green Future Party (GFP), National Democratic Party (NDP) da kuma Peoples Freedom Party (PFP).”
Ya kara da cewa a cikin su takwas biyu ne suka cika ka’idar da kundin tsarin mulki da dokar zabe suka saka na zama jam’iyar siyasa.

