
Majalisar dokokin jihar Taraba a ranar Alhamis ta yi watsi da rade-radin da ake cewa tana kokarin maye gurbin mataimakin gwamnan jihar, Aminu Alkali wanda yake kwance bashi da lafiya a birnin tarayya Abuja inda ya ke samun kulawar likitoci.
Shugaban kwamitin yada labarai na majalisar , Nelson Len shi ne ya yi tsokaci kan batun lokacin da yake magana da yan jaridu a Jalingo babban birnin jihar inda ya ce majalisar bata shirin tattaunawa kan batun.
Len ya bayyana cewa ana sa ran Alkali zai dawo bakin aiki da zarar ya warke sumul inda ya nemi jama’a da su yi watsi da rade-radin da ake yadawa cewa majalisar na shirin ayyana cewa Alkali ba zai iya gudanar da aikin sa ba saboda haka za a maye gurbinsa.
Ya kara jaddada cewa dukkanin bangarorin gwamnati uku da suka hada na majalisar, bangaren zartarwa da kuma na shari’a babu wanda ya fara daukar matakin cirewa ko kuma maye gurbin mataimakin gwamnan.
A cewarsa ana cigaba da kokarin ganin ya warke sumul ya cigaba da gudanar da ayyukansa.
Mataimakin gwamnan ya shafe tsawon lokaci yana jinya a gida Najeriya da kuma kasar Misra.