Akalla mutane tara ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu goma sha ɗaya suka jikkata sakamakon mummunan haɗarin mota da ya auku a garin Kyaramma, ƙaramar hukumar Ringim, a jihar Jigawa.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda ta jihar Jigawa, SP Lawan Shiisu Adam, ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, 7 ga Yuni, 2025.
A cewar sanarwar, haɗarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na dare (2:00am), lokacin da motocin Golf 3 guda biyu suka yi taho-mu-gama a yankin Kyaramma.
Motar farko mai lamba Kaduna MKA 687 AY, wanda Adamu Sunusi daga Hadejia ke tukawa, na kan hanyarta daga Abuja zuwa Gujungu, yayin da motar ta biyu mai lamba KWL 606 KA, da Bashari Danjummai daga Sauna, Jihar Kano ke tukawa, na kan hanyarta daga Hadejia zuwa Kano.
“Da suka isa Kyaramma, motocin suka yi karo da juna, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane tara, ciki har da direbobin duka motocin,” inji SP Shiisu.
An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gwamnati na Ringim, inda likitoci suka tabbatar da rasuwar fasinjoji tara.
An riga an gudanar da binciken gawarwaki, kuma an mika su ga iyalansu don yin jana’iza, yayin da ake cigaba da ƙoƙarin gano dangin sauran waɗanda suka rasu.
Yanzu haka, mutane goma sha ɗaya da suka jikkata suna kwance a asibiti, kuma suna samun kulawa.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Jigawa, CP AT Abdullahi, ya bayyana jimaminsa kan wannan mummunan lamari, tare da mika sakon ta’aziyya ga iyalan mamatan. Ya kuma yi kira ga direbobi da su guji gudu fiye da ƙima, tare da tabbatar da cewa motocinsu suna da ƙoshin lafiya kafin su hau hanya.
Hatsarin Mota Ya Halaka Mutum 9 Yayin Da Ya Jikkata 11 a Jihar Jigawa
