![](https://arewa.ng/storage/protesters-in-abuja2977156583117315281-1024x768.jpg)
Wasu masu zanga-zanga sun yi jerin gwano ya zuwa ƙofar fadar shugaban ƙasa da kuma majalisar dokokin ta tarayya kan dawo da Sarki Muhammadu Sanusi kan karagar mulkin jihar Kano.
A ranar Alhamis ne gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da dawo da Sanusi a matsayin Sarkin Kano bayan da ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautu ta jihar.
Majalisar dokokin jihar Kano ce tayi gyara kan dokar da tam ta raba masarautun jihar zuwa biyar ta kuma sauke Sanusi daga kujerarsa.
Duk da cewa wata kotu a jihar Kano ta bayar da umarnin cewa kada gwamnatin Kano ta aiwatar da kudirin dokar tuni gwamnatin ta yi gaban kanta ta naɗa Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 16 a daular fulani.
Da yake magana da manema labarai a yayin zanga-zangar ranar Juma’a, Abdullahi Saleh jami’in tsare-tsare na ƙungiyar Northern Nigeria Peace and Development Foundation ya ce gwamna Yusuf ya ɗauki matakin ne domin batawa wanda ya gada wato tsohon gwamna Ganduje.
Saleh ya ce ya kamata shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanya baki domin gudun karyewar doka da oda.