Wani mai safarar tabar wiwi ya fada hannun yan sanda a Kano

Rundunar yan sandan jihar Kano ta samu nasarar kama wani matashi da yayi safarar ganyen tabar wiwi daga jihar Edo zuwa jihare.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

Kiyawa ya ce jami’an rundunar na kar ta kwana karkashin jagorancin, CSP Hassan Nasir Jega su ne suka samu nasarar cafke mutumin a Garin Kwanar Dangora dake iyaka da jihar Kaduna, a karamar hukumar Kiru ta jihar.

Ya ce mutumin mai suna Agbor Victor dan shekara 30 ya ce yayi dakon tabar ne da darajarta ta haura miliyan daya domin kai wa wani Alhaji a cikin Kano, wanda tuni ya ranta a nakare

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]