2027:Jonathan ya ziyarci David Mark

A yayin da ake cigaba da hasashen takarar tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan a zaɓen shekarar 2027 sai gashi Jonathan ya ziyarci jagororin jam’iyar haɗaka ta ADC.

Ana ranar Alhamis ne Jonathan ya ziyarci shugaban jam’iyar ta ADC, David Mark a gidansa dake Abuja.

Ganawar na zuwa ne yan sa’o’in kadan bayan da gamayyar wasu yan siyasa da suka fito daga jam’iyyu daban-daban suka zaɓi jam’iyar ADC  a matsayin sabuwar jam’iyar da za su kalubalaci jam’iyar APC da ita a zaɓen 2027.

Tuni dai wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyar adawa ta PDP suka fara zawarcin Jonathan kan yazo ya yiwa jam’iyar takarar zaɓen shugaban a zaɓen 2027.

Kawo yanzu dai babu wata sakarwa da aka fitar kan abun da ganawar ta mayar da hankali akai.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]