Ɗan Ƙunar Baƙin Wake Ya Kashe Kansa A Kaduna

Wani mutum da ake zargin dan kunar baƙin wake ne a kungiyar Boko Haram ya tarwatsa kansa da bom a gidansa dake kan titin Ibrahim Haske a unguwar Keke dake karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Mutumin ya tashi bom ɗin ne domin gudun kada jami’an tsaro su kama shi.

Wasu majiyoyi dake unguwar sun ce jami’an tsaro sun dade suna sanya ido akan mutumin kafin daga bisani su bi sawunsa zuwa wani gida dake unguwar da ta Keke inda yake buya a ciki.

Wata majiyar ta bayyana cewa jami’an hukumar DSS, yan sanda da kuma sojoji su ne suka zagaye gidan inda suka riƙa musayar wuta bayan da ya fuskanci jami’an tsaron sun kusa cimmasa ɗan ta’addar ya tarwatsa kansa da bom.

An gano bindigar AK-47 tare da wasu bama-bamai biyu da basu fashe ba a gidan mutumin.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...