Ƴanta’adda Sun Kai Hari Kan Masu Jana’iza A Filato Inda Mutum Ɗaya Ya Mutu

Wasu masu ɗauke da makamai sun kai hari kan mutanen da ke rakiyar jana’izar wasu mutum biyu da aka kashe a ƙauyen Sol da ke ƙaramar hukumar Riyom ta Jihar Filato, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata wasu da dama.

Shugaban Ƙungiyar Berom Youth Moulders Association (BYM), Barrista Dalyop Solomon Mwantiri, ya ce maharan sun fara kai hari ne a daren ranar Laraba inda suka kashe wasu matasa biyu a ƙauyen Sol.

Ya ce da safiyar Alhamis, yayin da ake kai gawarwakin waɗanda aka kashe zuwa Babban Asibitin Riyom, maharan sun yi wa masu jana’izar kwanton bauna tare da bude musu wuta.

A cewarsa, wani mutum mai suna Toma Chuwang ya rasa ransa a harin, yayin da wasu da dama suka samu raunuka.

Ƙungiyar ta bukaci gwamnatin tarayya, gwamnatin Jihar Filato da hukumomin tsaro su ƙara yawan jami’an tsaro a yankin Riyom domin dakile ci gaba da hare-haren da ake fuskanta.

More from this stream

Recomended