Ƴan sanda sun kama mutum sama da 50 masu ɗiban ganima a Kano

A ci gaba da kokarin karfafa tsaron rayuka da dukiyoyi a jihar Kano, rundunar ‘yan sandan a ranar Juma’a ta ce an kama wasu karin mutane 57 da ake zargi da laifin sata da wawashe dukiyar jama’a a shaguna da kadarori da ake ruguzawa.

Wannan sanarwa ta fito ne cikin wata takarda da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna-Kiyawa ya fitar a yau.

“Kwamishanan ‘yan sandan ya yi gargadin cewa duk wadanda aka kama da irin wadannan laifuka za su fuskanci cikakken karfin doka.”

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]