A ci gaba da kokarin karfafa tsaron rayuka da dukiyoyi a jihar Kano, rundunar ‘yan sandan a ranar Juma’a ta ce an kama wasu karin mutane 57 da ake zargi da laifin sata da wawashe dukiyar jama’a a shaguna da kadarori da ake ruguzawa.
Wannan sanarwa ta fito ne cikin wata takarda da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna-Kiyawa ya fitar a yau.
“Kwamishanan ‘yan sandan ya yi gargadin cewa duk wadanda aka kama da irin wadannan laifuka za su fuskanci cikakken karfin doka.”