Ƴan Najeriya Uku Sun Shiga Hannun Jami’an Kenya Kan Zargin Zamba

Jami’an Kenya sun kama akalla ’yan Najeriya uku a Mwaliko Estate da ke Mwea Town bisa zargin wata makarkashiyar zamba ta yanar gizo.

Rahoton Tuko News ya nuna cewa rundunar Directorate of Criminal Investigations (DCI) ta cafke mutanen ne a ranar Laraba, bayan samun korafe-korafe daga mazauna unguwar game da abin da suka bayyana a matsayin mu’amalar dare wadda akwai tuhuma a ciki.

An bayyana sunayen wadanda aka kama a matsayin Peter Chukwujekwu, Alazor Chukulute Sunday, da Nnalue Chiagozie Samwe.

A cewar rahoton da aka fitar a ranar Alhamis, jami’an tsaro sun fatattake su daga cikin gidansu bayan alamu sun nuna akwai ayyukan da ba su dace ba da suke faruwa a wurin.

Rahoton ya ce mutanen sun yi ikirarin gudanar da kasuwancin yanar gizo, amma suna zaune a Kenya ba bisa ka’ida ba tare da samun lasisin aiki ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]