Ƴan Najeriya Uku Sun Shiga Hannun Jami’an Kenya Kan Zargin Zamba

Jami’an Kenya sun kama akalla ’yan Najeriya uku a Mwaliko Estate da ke Mwea Town bisa zargin wata makarkashiyar zamba ta yanar gizo.

Rahoton Tuko News ya nuna cewa rundunar Directorate of Criminal Investigations (DCI) ta cafke mutanen ne a ranar Laraba, bayan samun korafe-korafe daga mazauna unguwar game da abin da suka bayyana a matsayin mu’amalar dare wadda akwai tuhuma a ciki.

An bayyana sunayen wadanda aka kama a matsayin Peter Chukwujekwu, Alazor Chukulute Sunday, da Nnalue Chiagozie Samwe.

A cewar rahoton da aka fitar a ranar Alhamis, jami’an tsaro sun fatattake su daga cikin gidansu bayan alamu sun nuna akwai ayyukan da ba su dace ba da suke faruwa a wurin.

Rahoton ya ce mutanen sun yi ikirarin gudanar da kasuwancin yanar gizo, amma suna zaune a Kenya ba bisa ka’ida ba tare da samun lasisin aiki ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]