Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a.

‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun mamaye al’ummar Sabon-Gida da ke karamar hukumar Bungudu a jihar Zamfara.

Wani mazaunin unguwar Sabon-Gida mai suna Nazeer Sabon-Gida ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar garin ne da misalin karfe uku na safe inda suka fara harbe-harbe ba gaira ba dalili.

A cewarsa, an kai hari a dakunan kwanan dalibai uku, kuma ‘yan bindigar sun tafi da dukkan daliban da ke cikin dakunan kwanan dalibai.

“Sun shiga garin da misalin karfe 3 na safe kuma suka fara harbi ba kakkautawa,” in ji shi.

“Har yanzu ba mu tabbatar da adadin daliban da aka yi garkuwa da su ba saboda ‘yan bindigar sun shiga dakunan kwanan dalibai uku tare da yin garkuwa da dukkan daliban da ke wurin. Yana da wahala a iya tantance adadinsu a yanzu.”

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...