Wasu Æ´an bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille sakataren jam’iyar PDP na Æ™aramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.
Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro ya ce Æ´an bindigar sun harbe illa har lahira a gidansa da daren ranar Litinin.
Da aka tuntube shi domin karin bayani mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar Zamfara Yazid Abubakar ya ce zai tuntubi baturen Æ´an sanda kafin ya yi karin bayani.
Jihar Zamfara na cigaba da samun ƙarin hare-hare a ƴan kwanakin nan daga ƴan fashin daji dake ɗauke da makamai.
A cikin watan Maris ne gwamnan jihar Dauda Lawal Dare ya bayyana cewa a yanzu jihar ta zama cibiyar Æ´an fashin daji.