Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam’iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro ya ce ƴan bindigar sun harbe illa har lahira a gidansa da daren ranar Litinin.

Da aka tuntube shi domin karin bayani mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Zamfara Yazid Abubakar ya ce zai tuntubi baturen ƴan sanda kafin ya yi karin bayani.

Jihar Zamfara na cigaba da samun ƙarin hare-hare a ƴan kwanakin nan daga ƴan fashin daji dake ɗauke da makamai.

A cikin watan Maris ne gwamnan jihar Dauda Lawal Dare ya bayyana cewa a yanzu jihar ta zama cibiyar ƴan fashin daji.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]