Ƙungiyar ƙwadago ta dage sai anbiya 250,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Gamayyar kungiyoyin ƙwadago za su sake ganawa da shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu a cikin kwanaki bakwai domin cigaba da tattaunawa kan mafi ƙarancin albashi.

Da take magana da ƴan jaridar dake fadar shugaban ƙasa a ranar Alhamis, Nkiruka Onyejeocha ƙaramar ministar ƙwadago ta bayyana ƙwarin gwiwa cewa nan bada jimawa ba za a warware batun dambarwar mafi ƙarancin albashin.

Ministan na magana jim kaɗan bayan ganawar da shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya shugabannin kungiyar ƙwadago ta NLC da TUC.

Festus Osifo shugaban ƙungiyar TUC ya ce ganawar ta su ta mayar da hankali kan abubuwan da suka damu ƴan Najeriya.

Joe Ajaero shugaban ƙungiyar NLC ya ce ba wai an tattauna batun naira da kwabo a’a magana ake tsakanin naira 250,000 da kuma 62,000 a haka za a tsaya har sai an kawo ƙarshen tattaunawar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]