Ƴan sanda sun kama riƙaƙƙen ɓarawon awaki a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta ce jami’anta sun kama wani da ake zargin barawo ne da ya kware wajen satar awaki a kauyen Pasali Konu da ke karamar hukumar Kagarko a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansur Hassan, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya ranar Lahadi a Kaduna cewa an kama wanda ake zargin ne a ranar Asabar.

Hassan ya ce, a ranar 11 ga watan Nuwamba da misalin karfe 0430, wata tawagar sa ido da ‘yan banga, yayin da suke aikin sintiri a kauyen, sun kama matashin mai shekaru 20 da haihuwa.

A cewarsa, wanda ake zargin ya fito ne daga kauyen Igwa na karamar hukumar Kagarko.

“Wanda ake zargin, wanda ya kware wajen satar awaki, ya amsa cewa su biyu ne da suka zo kauyen domin satar awaki,” in ji Hassan.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama ƴan kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan ƴan sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan ƴan...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...