‘Yan Sanda Sun Kashe Wani Ƙasurgumin Ɗandaba a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana cewa ta kashe fitaccen ɗan daga da ake nema ruwa a jallo a jihar, Halifa Baba-Beru, wanda ya sanu wajen kai farmaki qa jama’a.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne ranar Litinin 22 ga Afrilu, 2025, da misalin ƙarfe 1 na rana, bayan samun kiran gaggawa dangane da wani harin fashi da aka kai a unguwar Gwammaja, karamar hukumar Dala, inda ake zargin Baba-Beru ya jagoranta.

A cewarsa, jami’ai biyu – CPL Abdullahi Ibrahim da S/C Yahaya Sa’idu – sun samu raunuka yayin musayar wuta, haka kuma shugaban ‘yan fashin, Baba-Beru, ya jikkata matuƙa.

Dukkansu an garzaya da su asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano, inda Baba-Beru ya rasu a yayin da ake masa jinya, yayin da jami’an suka samu sauki kuma aka sallame su.

Rundunar ta ce ta kammala bincike kan lamarin, kuma tana ci gaba da farautar sauran abokan aikin Baba-Beru.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]