Wani ya kashe kansa da matarsa da kuma dansa

Ƴan sanda a jihar Lagos, na tsargin wani mutum dan shekara 42 mai suna, Enifeh Omomo ya kashe kansa bayan ya kashe matarsa da kuma yaronsu dan shekara 6 a gidansu dake Ikorudu.

DSP Bala Elkana, mai magana da yawun rundunar yansandan jihar a wata sanarwa da ya fitar ya ce baturen yansanda na Ikorudu ya samu kiran kai daukin gaggawa ranar 24 ga watan Mayu da misalin karfe 8 na safe akan faruwar lamarin.

Elkana ya ce mutumin mazaunin gida mai namba 12 layin Eruga a unguwar Aga-Ikorudu ya kashe matarsa Faith Omomu mai shekaru 38 da kuma dansu Glorius Omomo.

“Lokacin da jami’ai masu binciken kisan kai suka isa wurin sunga gawar marigayin tana lilo a jikin fanka daure da igiya ya yin da gawar matar tasa da yaron ke kwance a kasa.

” An dauke gawarwakin ya zuwa babban asibiti domin binciken musabbabin mutuwarsu.Ana cigaba da gudanar da bincike,” a cewar sanarwar.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...