Ƴan sanda a jihar Lagos, na tsargin wani mutum dan shekara 42 mai suna, Enifeh Omomo ya kashe kansa bayan ya kashe matarsa da kuma yaronsu dan shekara 6 a gidansu dake Ikorudu.
DSP Bala Elkana, mai magana da yawun rundunar yansandan jihar a wata sanarwa da ya fitar ya ce baturen yansanda na Ikorudu ya samu kiran kai daukin gaggawa ranar 24 ga watan Mayu da misalin karfe 8 na safe akan faruwar lamarin.
Elkana ya ce mutumin mazaunin gida mai namba 12 layin Eruga a unguwar Aga-Ikorudu ya kashe matarsa Faith Omomu mai shekaru 38 da kuma dansu Glorius Omomo.
“Lokacin da jami’ai masu binciken kisan kai suka isa wurin sunga gawar marigayin tana lilo a jikin fanka daure da igiya ya yin da gawar matar tasa da yaron ke kwance a kasa.
” An dauke gawarwakin ya zuwa babban asibiti domin binciken musabbabin mutuwarsu.Ana cigaba da gudanar da bincike,” a cewar sanarwar.