A wane al’amari mai ban mamaki musamman duba da al’ada irin ta Malam Bahaushe, wata budurwa mazauniyar Sabuwar Ƙofa da ke Kano ta faɗa lambun soyayya inda ta tare zuwa gidan su saurayinta da take so ya aure ta.
Wani rahoto da Freedom Radio Kano ta sake a yau Lahadi ya nuno yadda budurwar take faɗin yadda take tsananin son wannan saurayi nata.
A cewar saurayin, ta faɗa son nasa ne tun lokacin da ya tare mata faɗa.
A daidai wannan lokaci kuma, Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta yi alkawarin shiga lamarin inda ta ce za ta duba yiwuwar taimakawa ganin sun yi aure.