Tinubu zai biya ƴan ASUU albashin wata 4 na lokacin da suka yi yajin aiki

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da biyan malaman jami’a ƴan ƙungiyar ASUU albashin wata huɗu cikin wata takwas ɗin da ba a biya su ba a lokacin da suka yi wani dogon yajin aiki.

Idan ba a manta ba, zamanin da Muhammadu Buhari yake shugaban ƙasa ƴan ƙungiyar sun yi dogon yajin aikin da ya fitar da ɗalibai daga hayyacinsu.

Wannan ya sa Shugaba Buhari a lokacin daukar matakin ƙin biyan duk wani ma’aikaci albashi muddin bai yi aiki ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]