Tinubu Ya Yaba Da Gudanar Da Zaɓukan Fidda Gwani A Jihohi



Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani a jihohin Najeriya, inda ya ce an shirya su cikin tsari da lumana.

Shugaban ya yi wannan jawabi ne a mazaɓarsa da ke Ikoyi bayan ya kaɗa ƙuri’a, inda ya ce tsarin ya nuna cewa dimokiraɗiyyar Najeriya na ƙara ƙarfi.

“Wannan shi ne siyasa, siyasa ta tun daga tushe, inda kowane mambar jam’iyyarmu ke da damar shiga zaɓen kamar ni ma yadda na zo na yi,” in ji Tinubu.

Ya ƙara da cewa ya yaba ƙwarai da yadda gwamnoni suka gudanar da tarukan jam’iyya a jihohinsu, tun daga matakin mazaɓa da ƙananan hukumomi har zuwa zaɓukan fidda gwani da tantance ‘yan takara.

More from this stream

Recomended