Tinubu Ya Jinjina Wa Nuhu Ribadu, Ya Ce Za A Murƙushe ‘Yan Ta’adda

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta yi nasara a yaƙi da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga da ke addabar al’ummar Najeriya.

Shugaban ya faɗi haka ne a ranar Litinin yayin da yake yabawa Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, bisa rawar da yake takawa wajen ƙarfafa tsaron ƙasa.

Tinubu ya bayyana Ribadu a matsayin mutum “mai gaskiya, jarumi, mai ƙarfin hali, kuma mai jajircewa a aikinsa.”

Yabon na zuwa ne a lokacin da shugaban ƙasar ya kai ziyara Jihar Adamawa State, inda ya nuna gamsuwa da jagoranci da ƙoƙarin Ribadu wajen inganta tsaro a faɗin ƙasar.

Haka kuma, Tinubu ya sake nanata ƙudirin Gwamnatin Tarayya na kawo ƙarshen matsalar tsaro a Najeriya, yana mai cewa ƙarƙashin jagorancin Ribadu, ƙasar za ta shawo kan ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]