Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da firaministan kasar, India Narendra Modi a ranar farko ta taron G20.
A ranar 4 ga watan Satumba ne Tinubu ya bar Najeriya domin halartar taron na kwanaki biyu a birnin New Delhi na India.
Ya yabawa India ta karbi bakuncin taron da kuma gayyatar Najeriya da aka yi.
Har ila yau shugaban kasar ya yi wata yar gajeriyar ganawa da shugabar tarayyar Turai, Ursula von der Leyen.