Sojojin sun ceto mutane da aka yi garkuwa da su a Borno

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta sun ceto wasu mutane uku da mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da su.

Rundunar ta ce an ceto mutanen ne a kauyen Firgi dake karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Litinin mai dauke da sahannun,Aminu Iliyasu.

Iliyasu ya ce an ceto mutanen ne sakamakon bayanan sirri da suka samu inda suka tsare yan ta’addar da har ta kai ga musayar wuta.

Ya kara da cewa sojojin sun kuma samu nasarar kwance bom da aka dana akan hanyar Bitta-Yamteke dake jihar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...