Sojojin sun ceto mutane da aka yi garkuwa da su a Borno

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta sun ceto wasu mutane uku da mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da su.

Rundunar ta ce an ceto mutanen ne a kauyen Firgi dake karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Litinin mai dauke da sahannun,Aminu Iliyasu.

Iliyasu ya ce an ceto mutanen ne sakamakon bayanan sirri da suka samu inda suka tsare yan ta’addar da har ta kai ga musayar wuta.

Ya kara da cewa sojojin sun kuma samu nasarar kwance bom da aka dana akan hanyar Bitta-Yamteke dake jihar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]