Sojoji sun kubutar da ‘yar bautar kasa daga wajen Boko Haram

Tun a watan Janairun wannan shekara ne aka sace ‘yar bautar kasan mai suna Halima Umar, a kan hanyar Goza zuwa garin Maiduguri. Wanda tun wancan lokacin babu ita ba duriyarta.

Rundunar sojin ta ce ta samu nasarar ceto matar ne sakamakon aikace-aikace da suke yi a dazuka, an dai mika matar ne ga gwamnatin jihar Borno.

Kwamandan rundunar sojin dake garin Maiduguri Birgediya Janar Bulama Biu, shine ya mika Halima ga mataimakin gwamnan jihar Borno Alhaji Umar Kadafur. Wanda kuma ya mika godiya da jinjina ga jami’an tsaron game da ayyuakan da suke gudanarwa a jihar.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...