Sojoji a birnin Ibadan  sun kama ƴan fafutukar kafa ƙasar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo.

Masu fafutukar sanye da kayan sojoji na  ƙasar waje kuma ɗauke da makamai sun farma sakatariyar gwamnatin jihar Oyo dake birnin na Ibadan.

Ɓullar labarin ke da wuya sojoji suka garzaya wurin inda suka yi wa sakatariyar ƙawanya inda suka samu nasarar kama su bayan da suka nuna turjiya ta hanyar musayar wuta.

Ƴan fafutukar sun buƙaci a gaggauta fara shirin ɓallewar yankin daga Najeriya domin kafa ƙasar ta Oduduwa.

More News

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naɗa Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...