Shugaban Sudan Ta Kudu Ya Sallami Manyan Mataimakansa Bayan Sunan Wani Mamaci Ya Fito Cikin Wadanda Aka Ba Wa Muƙami

Shugaban kasar Sudan ta Kudu, Salva Kiir, ya sallami wasu manyan mataimakansa biyu bayan wata badakala da ta biyo bayan nadin wani mutum da ya rasu shekaru biyar da suka gabata a matsayin mamba a kwamitin da zai jagoranci tattaunawa kan zaben da aka shirya gudanarwa a watan Disamba.

An bayyana sunan Steward Soroba Budia a cikin wata takardar umarnin shugaban kasa da aka fitar ranar 30 ga Janairu. Sai dai kafafen yada labarai na cikin gida suka nuna cewa Budia, wanda mamba ne a jam’iyyar adawa ta United Democratic Party (UDP), ya rasu tun shekaru biyar da suka wuce, lamarin da ya jawo suka da raha a kafafen sada zumunta.

Bayan faruwar lamarin, fadar shugaban kasa ta sanar da sallamar sakataren yada labarai na shugaban kasa, David Amour Major, da kuma babban jami’in gudanarwa a ma’aikatar harkokin shugaban kasa, Valentino Dhel Maluet. Sanarwar ba ta bayyana dalilin sallamar tasu ba.

A wata sanarwa da aka wallafa a shafin Facebook na shugaban kasa, Salva Kiir ya nuna godiya ga ayyukan da mutanen biyu suka yi a baya, tare da fatan alheri a gare su.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]