Shanu 18 sun mutu bayan sun ci ciyawar da aka yiwa feshin magani a jihar Filato

Shanu kusan 18 ne suka mutu bayan da ake zargin sun yi kiwo a wata gona da aka yiwa feshin magani a garin Vwei dake karamar hukumar Riyom ta jihar Filato.

A cewar wasu majiyoyi dake garin lamarin ya faru ne wajen karfe 12:00 na ranar Laraba lokacin da shanun mallakin wani mai suna Danazumi Haruna suka yi ratse cikin gonar da aka yiwa feshin magani.

Bakwai daga cikin shanun an samu damar yanka su nan take a yayin da 11 suka mutu nan take.

Karin wasu shanu 17 da abun ya shafa na can na samun kulawar jami’an kula da lafiyar da dabbobi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]