Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdulaziz ya kira taron gaggawa na Kasashen Kungiyar Musulmi ta OIC.
Kungiyar ta OIC ita ce kungiya mafi girma bayan majalisar dinkin duniya inda take da kasashe mambobi sama da 50 da suka fito daga nahiyoyi da daban-daban.
A wata sanarwa da aka wallafa a shafin intanet na kungiyar ta OIC ta ce taron zai gudana ranar 18 da kuma 19 ga watan Satumba a birnin Jedda na kasar Saudiya
An kira taron na gaggawa ne domin tattauna rikicin da ake tsakanin kasar Isra’ila da kungiyar Hamas.