Rooney zai fuskanci Man United a FA Cup | BBC News

Rooney

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wayne Rooney zai fuskanci tsohuwar kungiyarsa, Manchester United a wasan zagaye na biyar a FA Cup.

Kungiyar Rooney ta yi nasarar doke Northampton a wasa na biyu a zagaye na biyar a FA Cup.

Mai rike da kofi Manchester City za ta ziyarci Sheffield Wednesday.

Chelsea za ta karbi bakuncin Liverpool wadda ta fitar da Shrewbury a wasa na biyu da suka sake, Arsenal ta ziyarci Portsmouth.

Dukkan wasanni takwas za a yi sune a tsakiyar mako wato 3 zuwa biyar ga watan Maris.

Rooney, ya koma Derby mai buga gasar Championship a matsayin koci kuma dan wasa a watan Janairu daga DC United.

Mai shekara 34, ya buga wa United wasa 559 ya kuma ci kwallo 253.

Ya kuma lashe Champions League da Europa League da FA Cup tun bayan da ya koma Old Trafford da taka leda daga Everton a 2004 kan fam miliyan 27.

Tun bayan da ya bar Old Trafford sau biyu yana fuskantar United, bayan da ya koma Everton, amma dukkan karawar rashin nasara suka yi a kakar 2017/18.

More News

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...