Liverpool ta samu nasarar doke Aston Villa har gida da ci 2-1 bayan kwashe kusan minti 93 ana fafatawa.
Tun da fari Trezeguet ne ya ci wa wa Aston Villa a minti na 21 da fara wasan, yayin da Andy Robertson ya farke wa Liverpool kwallonta a minti 87.
Ana gab da tashi daga wasan ne kuma Sadio Mane ya kara ta biyu, wadda da ita ne Liverpool ta ci gaba da zama a saman teburi.
Har yanzu dai Liverpool ce ke ci gaba da jan ragamar gasar Premeir da maki shida tsakainta da Manchester City da ke biye mata.
Liverpool dai na yawan samun nasarar jefa kwallo bayan minti 90 da fara wasa. Kwallon da Sadio Mane ya ci ita ce ta 35 da kungiyar ta ci bayan cikar minti 90 na wasa, sama da kowace kungiya kenan a Premier da kwallo 10.
Liverpool za ta karbi bakuncin Manchester City ne a wasa na gaba kafin daga bisa ni ta je Crystal Palace, inda ake ganin wadannan wasanni a matsayin wadanda za su kawo wa Livepool kalubale.