Okorocha ya yi kira da a kama Ahmad Gulak

Gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha ya yi kira da a kama Ahmad Gulak, shugaban kwamitin gudanar da zaben fidda gwani yan takarar gwamna a jihar.

Hope Uzodimma da kuma Uche Nwosu sune mutanen da aka bayyana a matsayin wanda suke lashe zaben mai cike da rudani.

Shugabancin jam’iyar APC na kasa ya soke zaɓen da aka gudanar kana ya wargaza kwamitin.

Gulak ya bar jihar a wani yanayi dake cike da sarkakiya abin da ya tilastawa reshen jam’iyar na jihar ya bayyana bacewarsa.

Amma da yake bayyana sakamakon zaben a birnin tarayya Abuja, Gulak ya ce Sanata Hope Uzodimma shine ya samu nasara a zaben da gagarumin rinjaye inda ya a zargi Okorocha da yinkurin yin garkuwa da shi.

Ya ce anyi garkuwa da sauran yan kwamitin su 9 bisa umarnin gwamna Rochas Okorocha zargin da Okorocha ya musalta a cikin sanarwar da Sam Onwuemeodo, ya fitar a madadinsa.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...