NLC da gwamnatin Najeriya sun cimma yarjejeniya kan albashi

Bayan ganawar sa’o’i shida a ranar Litinin, gwamnatin Najeriya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da kungiyar kwadago bayan da gwamnati ta yi alkawarin cewa shugaba Bola Tinubu ya kuduri aniyar biyan mafi karancin albashi na sama da N60,000. 

Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume ne ya sanar da hakan bayan kammala taron da shugabannin kungiyoyin kwadago suka yi a Abuja wanda aka fara da karfe 5 na yamma kuma aka kammala ‘yan mintoci zuwa karfe 11 na dare.

Ya ce shugaban kasar ya “yi alkawarin biyan mafi karancin albashi na kasa wanda ya haura N60,000”.

Rahotanni sun nuna cewa kungiyar kwadagon da ta kunshi kungiyar kwadago ta Najeriya da kuma kungiyar ‘yan kasuwa ta bayyana yajin aikin sai baba-ta-gani a fadin kasar sakamakon gazawar gwamnatin tarayya wajen biyan ma’aikatan Najeriya albashi.

 

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]