Nenadi Usman ta zama sabuwar shugabar riko ta kasa ta jam’iyar LP

Wani tsagi na jam’iyar Labour Party ya nada Nenadi Usman a matsayin shugabar riko ta jam’iyar.

An zabi Usman ne biyo bayan wani taron shugabannin jam’iyar da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja

Darlington Nwokocha tsohon sanata mai wakiltar mazabar Abia ta tsakiya shi ne wanda aka zaba a matsayin sakataren riko na jam’iyar.

Nadin da aka yi wani bangare ne na kokarin da tsagin yake yi na sake samarwa da jam’iyar shugabanni gabanin zaben sabbin shugabannni a wurin babban taron jam’iyar na kasa da za ayi.

Ana saka ran sabon shugabancin rikon da aka samar zai jagoranci ayyukan jam’iyar har sai an zabi sababbin shugabannin a wurin babban taron jam’iyar na kasa.

A yayin taron na ranar Juma’a shugabannin jam’iyar sun amince da jadawalin gudanar da zaben shugabannin jam’iyar a matakin mazabu, kananan hukumomi, jihohi da kuma shiyoyi da kuma na kasa baki daya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]